Abban Sojoji Takun Karshe Chapter 92 – Hausa Novels (2024)

Join this link to follow my tiktok acct👇https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖**Father of soldiers**🔥TAKUN ƘARSHE🔥*_❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana ta whatsapp dan Allah banda kiran wayar,bana ɗagawa 08103884440❤_Nagode da shawararki Aunty azmee,in sha Allah zanyi amfani da ita” “Yawwa haka nake son ji” azmee tayi maganar tare da komawa cikin kitchen,Sehrish kuwa bata wuce part ɗinshi ba,bedroom ɗinsu ta wuce,sam takasa samun natsuwa,ta rasa shawarar wa zata ɗauka acikinsu,bakomai yafi sata fargaba ba,fa ce abunda zai biyo baya idan tayi kuskuren zuwa sashen shi,Har wuraren ƙarfe goma sha biyu na dare bata runtsa ba,tana zaune saman gadon nasu,yayin da wayarta ke ruƙe a hannunta,Hosana na kwance a gefenta tana bacci cikin bargo hankalinta kwance,Jahad kuma na can ɗakin azmee,

Wani tunani ne yazo mata acikin zuciyarta,da sauri ta shiga contacts ta lalubo layin Aunty azeema,ta danna mata kira,cikin sa’a ta ɗaga kiran nata, Kara wayar tayi a kunnanta,tare da yi mata sallama, “Assalamu Alaikum,”Aunty azeema tace”Wa’alaikum salam daughter,me kikeyi har yanzu baki yi bacci ba,”? “Na kasa yin bacci ne,ina cikin damuwa”acewar Sehrish, Azeema tace”kodai duk fargabar babban yayan naku ne?”Ba haka bane,Aunty azeema,na ɗan shiga damuwa ne,yau babban yaya bai fito daga part ɗinshi ba,har akayi sallar La’asar da magrib,bai fito ba,” Maganar sehrish ta ɗan tashi hankalin hajiya azeema, “Amma ya ci abinci kuwa”?Sehrish tace”baici abincin gida ba,ɗazu dai yasa an kawo mashi abincin restaurant,amma bani da masaniya akan yaci ko bai ci ba,” Shiru hajiya azeema tayi na wani dan lokaci,haka itama sehrish ɗin,Kowa da abunda yake saƙawa aranshi,

“Kina jina”muryar hajiya azeema ce ta katse mata zancen zucin da ta shiga, “Ina sauraronki Aunty,””Gaskiya akwai matsala,saboda ba ƙaramin abu bane zai hana Sgr zuwa masallaci ba,Ina da tabbacin cewa zuciyarshi ta motsa,Allah kaɗae yasan halin da yake ciki,gashi babu kowa agidan idan baku ba,dama ace su Abbanku suna nan ne ko Omar zasu iya shawo kan matsalar,Amma yanzu haɗari ne wani ya tunkare shi,tunda ba’asan halin da yake ciki ba,wani irin zafin zuciyane dashi idan ya fusata kowa tsoran tunkararshi yake yi,Amma idan akaci sa’a,Ya yanke jiki ya faɗi ya suma a lokacin da zuciyar tashi ta motsa,to tabbas koda ya farfaɗo bazai tashi da wannan fushin ba……”dakatawa ta ɗan yi da yin maganar,tana sauke ajiyar zuciya, “Yanzu ya zamuyi kenan”?sehrish ta tambaya,fuskarta dauke da damuwa, “Abunda za’ae yanzu shine,inaso kije part ɗin nashi kiga a wani hali yake ciki,Amma fa kada ki bari ya ganki,a 6oye zaki je,in ba haka ba a tsinto ƙasusuwanki a dakinshi,”ta karasa maganar cike da zolaya,

Related Articles

Dariya sehrish ta dan yi duk da tsoron daya kamata,bayan ta tsagaita da yin dariyar tace”Shikenan Aunty azeema,zanje in sha Allah,” Azeema tace”yawwa daughter,idan kin dawo duk abunda ya faru ki sanar dani pls,” “Toh Aunty,”Daga nan sukayi sallama,saukowa daga saman gadon Sehrish tayi,bayan ta ajiye wayar saman side drawer,ta zura slipper ɗinta dake ajiye nan ƙasan,ta gyara mayafin jikinta sannan ta fito daga dakin nasu, Tunkafin ma ta hau upstairs din gabanta ke faɗuwa rass rasss,tamkar wadda zata tunkari wani zombie,A hankali take taka staircase ɗin harta samu ta haura sama,tana tafiya tana ambaton”La’ilah ha illa antas subhanaka inni kuntu minazzalimin,”har tazo bakin ƙopar part dinshi,kamar wata 6arauniya haka ta leƙa cikin falon,ganin baya ciki yasa ta sauke ajiyar zuciya,cikin sanɗa ta zura ƙafarta ciki,a hankali take tafiya,gudun kada yaji sautin takalminta yasa ta zuƙunna tare da ciresu ta ruƙesu a hannunta,A ƙopar bedroom ɗinshi ta tsaya,har lokacin bata daina ambaton La’ila ha illah anta subhanala inni kuntu minazzalimin,acikin zuciyarta ba,saboda tsabar tsoro,zuciyarta tamkar zata fito daga ƙirjinta,saboda bugun da take yi mata,daraam!daraaam,

A hankali ta ɗan zura kanta tare da leƙawa cikin ɗakin nashi, Kwance yake saman gadon,gangar jikin na asaman gadon,yayin da head ɗinsa zuwa wuyanshi suka zuro daga gefen gadon,Sumar kanshi ta zubo har saman floor, Gabanta ne ya faɗi rasss!tun daga kan yadda yayi kwanciyar ta gane cewa babu lafiya,gaba ɗaya zufa ta wanke jikinshi tamkar wanda ya watsa ruwa ajikinshi,ta ko’ina zufar ke tsastsafo mashi,gaba ɗaya ga66an jikinshi sun sake, Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,batasan ko bacci yake yi ba,ko suma yayi,Allah wa’alamu, Zura ƙafarta tayi yayin da gabanta ke ci gaba da faduwa,Shiga cikin bedroom ɗin tayi,har zuwa wurin gadon nashi,Yanayin kwanciyar tashi ma,Zata iya haifar mashi da matsanancin ciwon wuya,saboda yadda ya yi sadda kai, Zuba mashi ido tayi tana kallon fuskarshi,daga gani ba ƙaramin jiki yaji ba,

Tunani ta shiga yi,kodai ta ɗaukko ruwa ta yayyafa mashi,duk da bata da tabbacin cewar ko suman yayi ne,amma ga dukkan alamu ya suma ne…… , Da sauri ta juya ta koma palour,fridge ta nufa da sauri sauri ta buɗe shi ta ɗauko robar ruwa,Sannan ta dawo cikin ɗakin nashi,Tashin hankali,Tsayawa tayi tana tunanin taya ma zata fara yayyafa mashi ruwan batare daya ganta ba?kyau tana watsa mashi ta watsa da gudu kafin ya murmure, Jikinta sae kerma yake yi,a haka ta buɗe robar ruwan,ta tarfa ruwan a hannunta,Ja da baya ta ɗan yi,sai da taba da interval sosai a tsakaninsu,daga inda take ta yarfa mashi ruwan akan fuskarshi,yaraf!ya saukar mashi,Aikuwa nan take ya shiga sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya,da gudun gaske sehrish ta 6oye acikin labulen ɗakin nashi,zuciyarta na ɗar ɗar, Sannu a hankali ya buɗe blue eyes ɗinshi,yana faman sauke ajiyar zuciya,bin kasan bedroom ɗin nashi yayi da kallo,kafin yayi yunƙurin mayar da kanshi saman Gadon nashi,saman pillow ya aza kanshi,yasa hannu yana murza wuyanshi saboda raɗaɗin da ya ji a wurin,lumshe idanuwanshi yayi tare da sake buɗesu,jikinshi babu ƙwari amma zazza6in ya sauka daga jikinshi,dakyar ya iya miƙewa daga zaune,ya jingina bayanshi a head board ɗin gadon,Yayin da idanuwanshi ke a lumshe,

Sehrish dake 6oye bayan curtains ɗin ɗakin,tana jin duk wani moving ɗinshi,ta toshe bakinta da hancinta da tafin hannunta,saboda gudun kar ya gane akwai mutun aɗakin nashi, Almost 15 mins yana a zaune bai motsa ba,tun da yake a arayuwarshi bai ta6a shiga matsanancin halin daya shiga ba irin na yau,kamar wani mara gata,sae kace ba Surgeon General ba,Yau ya ɗanɗani zafin kadaici,duk a sanadin kalaman da sehrish ta gaya mashi, Saukowa yayi daga saman gadon,Ya tsaya atsaye tare da sanya hannu ya tu6e shirt ɗin dake ajikinta,Yayi wurgi da ita saman gadon,Zame belt ɗin wandonshi yayi ya jefar dashi saman rigar,sannan ya zame dogon wandon,Ya rage daga shi sai short light blue, yana tafiya cike da rashin ƙwarin jiki,a haka har ya buɗe toilet ya shige ciki,Sehrish na jin motsin buɗe kopar toilet,Jiki na rawa ta lalla6a,saɗaf saɗaf ta fito daga cikin bedroom din,Hannunta riƙe da bottle water din,Saman fridge ta ajiye robar ruwan sannan ta kama hanyar fita daga falon,Har ta kai bakin kopar dakin ta juyo ta kalli kayan Breakfast ɗin da Armstrong ya kawo mashi,nan ta gane cewa bai ci komai ba, Fitowa tayi daga part ɗin nashi,ta saukko downstairs da sauri ta nufi ɗakinsu,bayan ta shiga ciki ta ɗauki wayarta,tare da danna ma Aunty azeema kira,nan take ta ɗaga kiran,

Da sauri ta sanya wayar a kunnanta,tun kafin tayi magana Hajiya azeema tace”Ya ake ciki ne? Sehrish tace”Naje part ɗin nashi,na same shi a sume saman gadonshi,gaskiya ba ƙaramin jiki yaji ba,nasamu dae na yayyafa mashi ruwa batare da ya ganni ba,na lalla6a na fito daga ɗakin nasa,naji ya shiga toilet da alama wanka zaiyi,Amma fa naga kayan abincin da aka kawo mashi daga restaurant,Da alama bai ci komai ba,” Hajiya azeema tace”Good!,naji daɗi da bai ganki ba,Kuma naji daɗin suman nan da yayi,saboda zai samu sauƙi acikin zuciyarshi,duk da nasan dole ya ƙullace ki a aranshi,” Murmushi sehrish ta ɗan yi kafin ta kuma cewa”duk yau baici komai ba,””Kada ki damu da wannan,ita yunwa bata da hankali,Ina nan dake wannan abincin da ya bari wanda aka kawo mashi na restaurant,Shi zai nema ina nan dake,yanzu dae ki kwanta kiyi bacci’, Hankalin sehrish ba ƙaramin kwanciya yayi ba, “Ki kwanta kiyi bacci,Sae Allah ya kaimu gobe zamuyi magana,” sallama sukayi da ita,Sehrish ta kwanta saman gadon tare da ajiye wayarta saman stomach ɗinta,yayin da idanuwanta ke fuskantar ceilling ɗin dakin,Sgr kuwa,bayan ya fito daga wankan da ya shiga,jallabiya ya zura ajikinshi ash colour,har wani jiri yake gani saboda tsabar yunwar da ya ke ji,ba arziƙi ya dawo palour saman sofa ya zauna,tare da kai hannu ya ɗauki burger ɗin nan,da ya ajiye saman table,Turata yayi cikin bakinsa ya shiga cin ta har yana shaƙewa,a ƙa’ida baya cin abincin da ya sha iska wanda aka bari a buɗe,Amma yau ba kanta,Ci kawai yakeyi,tass ya cinyeta,Miƙewa yayi da sauri ya nufi wurin fridge don ya daukko drink din da zaisha,hannu yakai tare da ɗaukar bottle water ɗin da Sehrish ta bari asaman fridge ɗin,6alle marfin yayi ya kafata a bakinshi yana kwankwadar ruwan,sae da yayi rabin ruwan dake acikinta,sannan ya dakata da shan ruwan da yake yi,Sai lokacin ya ankara da inda ya ɗauki robar ruwan,Shiru ya ɗan yi tare da zubawa robar ruwan dake hannunshi ido yana kallonta,Shi dai yasan bai ajiye ruwa asaman fridge ba,tunani ya shiga yi,Yanayin yarda ya farka duk da akwai zufa ajikinshi,amma tabbas yaji Saukar ruwa akan fuskarshi wannan ya tabbatar mashi da cewar wani ya shigo cikin part ɗinsa,Hannu yasa tare da buɗe fridge ɗin ya saka robar ciki,Sannan ya ɗauki co*ke mai sanyi, Komawa yayi saman sofa din,ya zauna tare da kai hannu ya buɗe daya daga cikin ledojin,take away ya curo ya buɗe shi Chips ne aciki duk yayi sanyi,amma ahaka ya shiga turashi acikin bakinshi yana ci,bai ta6a shiga yanayi irin wannan ba a rayuwarshi,tass ya cinye duk wani abu dake a wurin,bayan ya kammala cin abincin,mikewa yayi ya koma cikin bedroom ɗin shi,ya ɗauko wayarshi,Sannan ya dawo saman sofa ɗin ya kwanta tare da miƙar da ƙafafunshi saman hannun kujerar,

Zubama screen ɗin wayar ido yayi yana kallonshi batare da ƙyaftawar ido ba,yama rasa wa zai kira yaji sanyi aranshi,numbar Abbansu ya lalubo ya danna mashi call,Ringing din farko Abbansu ya ɗaga kiran nashi muryarshi da alamun bacci yace”My son,Me kake yi har yanzu baka yi bacci ba”? batare da ya amsa mashi tambayarshi yace”Daddy,when zaku dawo?gida duk ba daɗi,” Tsananin mamakine ya kama Abbansu,Yau Sgr da kanshi yake cewa Gida babu daɗi saboda basu nan,ta wani 6angaren kuma yaji daɗin hakan sosai, “Kayi missing ɗinmu ne”?Abba ya tambayeshi,muryarshi akasalance yace”Yeah,especially you,I missed u so much,” Farin ciki ne ya cika Abbansu,kamar ya janyoshi ta cikin wayar ya rungumeshi, “Pls Daddy,just come back home,if not zan biyoku damaturun ne,in yaso saimu dawo atare,” Sgr na jiyo sautin muryar Abbansu yana tiƙar dariya, “Are u laughing at me”?Tsagaitawa Abbansu yayi da yin dariyar yace”dole nayi dariyar Farin ciki mana,Yau ya kasance rana ta farko daka nuna kayi kewarmu sosai,naji muryarka wani iri tamkar zaka yi kuka,tell me what’s wrong with u,wani ya ta6a mun kaine”?

Sgr yace”bana jin daɗin zuciyata ne,ko zaka sanyani farin ciki? Abba yace”yanzun nan kuwa,bari na tuna maka wani abu,lokacin da kana ɗan jinjiri dakai cikin towel,kyakkyawa da kai,Na ƙwallafa rai sosai akan ka, kai kuma ga kyuyar tsiya,ka ƙi jinin baƙin mutun ya ɗauke ka,koni da nake mahaifinka ban isa na ɗauke ka ba,in ba bacci ya ɗaukeka ba,Sae in lalla6a in shiga ɗakinka,In zauna saman gadon in zuba maka ido inta kallonka,araina ina cewa Yanzu wannan mallakina ne,Allah ya bani Halak malak,Haka zan tasaka gaba ina kallonka,da zarar ka farka kuwa,mukayi ido biyu,kamar kaga wani 6arawo haka zaka fasa ihu kana ambaton sunan Mommynka,” Lumshe ido Sgr yayi yana sauraron Abbansu,fuskarshi asake tamkar zaiyi murmushi,wata irin natsuwa yaji acikin zuciyarshi, “Amma daga baya,saboda irin kulawar da nake baka sae ka gane cewa ni mahaifinka ne,kuma inason ka sosai fiye da kowa,sae gashi da kanka,kake zuwa wurina don in ɗauke ka,mu tafi yawo atare,” jikin Sgr ba ƙaramin sanyi yayi ba,kalaman Abbansu sunyi matuƙar ta6a mashi zuciya, “Amma ni sai inga kamar baka sona,baka damu dani ba kamar yadda na damu da kai….”

Tunkan ya ƙarasa maganar Sgr ya katse shi da cewa”Daddy kadaina faɗan hakan bana jin daɗi,duk duniya bani da tamkarka,kaine mahaifina,Jigona kuma ginshiƙi na,Abun alfaharina,madubin dubawana….”. Wani irin farin cikine ya lullu6e Abbansu,bai ta6a jin irin wannan yabon daga bakin Sgr ba,sai yau har ya fara tunanin anya kuwa cikin hayyacinshi yake gaya mashi waɗannan kalaman?ko kuwa ya ɗan kora wani abune,Gashi ya saki jiki sai surutu yake yi mashi kamar ba wannan miskilin ba…” “Pls Rafayet,ka maimaita mun kalaman nan daka faɗamun,inaso nayi recording ɗinsu,” fashewa da dariya Sgr yayi,hakan ba ƙaramin ɗaurewa Abbansu kai yayi ba, Cike da mamaki yace”Rafayet,dariya kakeyi mun,dan Allah faɗamun kodai kasha kwaya ne yau,” “Daddy bansha komai ba,lafiyana ƙalou,kawai ina jin daɗin waya da kaine,ka bari idan ka dawo gida zan sake maimaita maka sai kaji a kunnanka,” Cikin raha sukayi wayar gwanin ban sha’awa hira irin ta da da mahaifi suka yi wadanda suke cikin begen juna,a karshe sukayi sallama,sauke ajiyar zuciya yayi tare da aza wayar saman chest ɗinshi,wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarshi,still kalaman Sehrish nadawo mashi acikin ranshi,waɗannan kalaman dae su suka fi ta6a mashi zuciya,Mara tausayi mara Imani,da kuma danganta shi da ya sayyadi,Tariyo abunda ya faru tsakaninsu ya shiga yi cikin ranshi,Yadda ya damƙo wuyan rigarta tare da yin wurgi da ita ta bugi bango,har ta fashe da kuka saboda zafin da taji,da kuma munanan kalaman da ta jefa mashi,da alama nazarin wani abu yake yi,dangane da abunda ya faru jiya atsakaninsu,Ya jima asaman Sofa ɗin,kafin daga bisani ya koma cikin bedroom ɗinshi,darduma ya dauƙo ya shimfiɗa tare da kabbara salla,Sae da ya fara biyan bashin sallolin da baiyi ba,sannan ya ɗaura da yin nafilfilin daren daya saba yi,bayan ya kammala ya ɗauki qur’ani ya shiga karantawa,nan take yaji natsuwa tazo mashi acikin zuciyarshi,bashi ya kwanta bacci ba,har sae wuraren ƙarfe biyu na dare,sannan ya haye saman gadonshi ya kwanta,bacci 6arawo yayi awon gaba dashi,Itama Sehrish,sae da tayi sallar daren,kafin ta kwanta bacci,Abunda ya faru daren jiya da Aunty babba ta zauna zaman jiran Hayaam….

tunda ƙarfe goma ta buga hayaam bata dawo ba,nan hankalinta yayi mugun tashi,fitowa tayi daga bedroom ɗinsu,ta shiga zarya acikin hotel ɗin,ko Allah zaisa taga gifcinta,amma shiru babu ita har receptionists taje ta tambaya ko sunga fitarta suka tabbatar mata da basu ganta ba,ƙarshe da ta gaji da biɗiɗin nemanta,komawa tayi ɗakin nasu zuciyarta a ƙuntace ta kwanta,duk da halin da ta shiga na rashin hayaam,hakan bai hanata yin bacci ba,harda minshari, Haroon kuwa tun da ya kammala yi mata wannan aika aikar,ya tattara yabar Hotel ɗin ya gudu gaba ɗaya,don kuwa daƙyar in hayaam zata ƙara moruwa,Ya naƙasata sosai,a saman gadon ya barta a yashe,Wuraren Sallar asuba,Wayar Aunty babba dake ajiye gefenta ta soma ringing,can cikin bacci ta dinga jin ringing ɗin wayar,dama ta kwana da tunanin hayaam zata iya kiran ta in ta buɗe wayarta,hakan yasa ta farka da sauri takai hannu ta ɗauki wayar,duba screen ɗin wayar tayi da 6oyayyiyar lamba aka kirata,cike da mamaki tace”To fa,waye ya kirani a irin wannan lokacin da 6oyayyiyar number?kodai hayaam ce ta kira,bari na ɗaga na ji, Picking call ɗin tayi ta kara wayar a kunnanta,

Tun kafin tayi sallama taji ance”Madam,barka da warhaka” gabanta ne ya ɗan faɗi rass,amma ta dake tace”yawwa,dan Allah wanene ke magana,” “Babu bukatar ki sani,dama na kira ne don in yi aikin lada,Nasan kina ta neman hayaam ido a rufe,to hayaam dae a halin yanzu addu’arki take buƙata,idan kina son sanin inda take,yanzu zan turo maki da message na address ɗin inda take,sae ki hanzarta zuwa don ki kai mata agaji,Allah ya bata lafiya,idan ta samu ciki dan Allah a ajiyemun abuna,inaso” yana faɗin haka,yayi rejecting kiran,” Waro ido waje Aunty babba tayi,a hargitse ta saukko daga saman gadon hannunta riƙe da wayar,jikinta har kerma yakeyi,zarya ta shiga yi acikin ɗakin tana jiran shigowar saƙon, A fili tace”Allah yasa dae hayaam ba wani taje taba ma kanta ba yayi amfani da ita,Sae da naja mata kunne akan ta daina kula maza,amma da ya ke karya ce gaya nan tana son ja mun bala’e,ina zaman zaman lafiyana,”Tana cikin wannan zullumin,taji ƙarar shigowar message da sauri ta duba top of the screen ɗin wayar,

“Vip,Room 34,”shine abunda taga an rubuta acikin message ɗin,kuma babu numbar wanda ya tura,anyi hidden number, Sai da tayi zurfin tunani sannan ta gane cewa numbar ɗakin hotel ne aka turo mata,hakan na nufin cewa hayaam tana acikin hotel ɗin, Jiki na rawa ta ƙarasa wurin trolley ɗin kayansu dake ajiye,gefen wardrobe,buɗe wa tayi ta dauko mayafi ta lullu6a asaman kanta, Sannan ta tura kopar ɗakin ta fito,tafiya takeyi cike da zullumin abunda zai biyo baya,sae bin ɗakunan dake a wurin takeyi tana bin numbobin jikinsu,cikin sa’a batare da tasha wahala ba tazo kan numbar ɗakin da aka turo mata,sae da ta duba dakyau taga Room 34 ne,Hada key aka ajiye mata ajikin ƙopar,wannan ya tabbatar mata da cewa da gangan aka sanya key ɗin,saboda in tazo ta buɗe ta shiga, Gabanta sae faɗuwa yakeyi,a hankali ta sanya hannunta ta ɗan murza key ɗin ɗakin ya buɗe,cike da fargaba ta tura ƙopar ɗakin a wani slow kopar ta soma buɗewa ƙiiiiiii,tun kafin ma ta sanya kafarta acikin ɗakin ta hango pant yashe a saman tiles,Rass taji gabanta ya faɗi,wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,dakyar ta shiga cikin ɗakin,karaf Idanuwanta suka hango mata Bra din hayaam dake sagale ajikin mirror,tun daga nan tasha jinin jikinta,wurga idonta tayi gefen hagunta,Handbag ɗin hayaam ta hango yashe a kasa,da alama wurgi akayi da jakar kayan cikinta suka watse akasa,hada wayarta ma duk screen ɗin ya fashe,

..arazane Aunty babba takai idonta saman gadon,mutunne a kwance an lullu6e shi da bargo, A tsananin tsorace ta ƙarasa gaban gadon,sanya hannunta tayi tare da zame bargon a hankali,tana buɗe bargon da sauri ta mayar ta rufe,saboda tashin hankalin da ta gani,hannu ta aza akai ta fasa ihu tana faɗin”Nashiga uku!Wayyo Allah na,Hayaam wani marar imanin ne yayi maki wannan aika aikar!hayaam waye ya yashe ki haka!La’ila ha’illallahu muhammadur rasulillahi!Amma kowaye wannan anyi haihuwar asara,Uwarshi ta haifo mana Bala’e” ta inda take shiga bata nan take fita ba,Muryarta har shaƙewa takeyi saboda tsabar baƙin ciki,tamkar ta haɗiyi zuciya ta mutu,..a karshe ta fashe da matsanancin kuka,tare da hayewa saman gadon,tana cigaba da sambatu,da alama ta fara zaucewa, “mun shiga uku mu yau,Wllh dana san haka zata faru da bamu zauna a hotel ɗin nan ba,ƙaddara ce kawai ta riga fata,Hayaam kowaye wannan ya gama damu,ɗan jarin da muke taƙama dashi ya kwashe komai babu,ya yashe ki,ya karya mana tattalin arziƙin da yayi mana saura,Ya takaita mu don ubanshi,wlh koma wani jarababben ne,Sae Allah ya toni asirinshi,Ni na ta6a ganin jaraba irin wannan,bai bar komai ba,yayi mata wanwar ɗan jakar uban,haihuwar asara haihuwar titi,haihuwar kwararo….”kasa ƙarasa maganar tayi,wani irin ƙululun baƙin cikine ya tokare mata maƙoshinta,nan tashiga yin kakarin amai,ta saukko daga saman gadon agalabaice ta nufi toilet ɗin cikin ɗakin ta shiga,Sosai tayi amai tamkar ƴan hanjin cikinta zasu fito waje,ta jima acikin toilet ɗin kafin ta fito,tana tafiya ƙafafunta na harɗewa,

Fitowa tayi daga ɗakin ta koma ɗakinsu,Trolley ɗin kayansu ta buɗe,Jallabiya ta ɗaukowa hayaam tare da Mayafi,Sannan ta koma can ɗakin,taci wahala haka ta kinkimi hayaam ta shiga da ita toilet,wani wurin ma ajikinta,baya ta6uwa sae dai anje asibiti duk ya jagule babu kyan gani,hatta la66anta duk sun faffashe hada busasshen jini,nipple ɗinta na right breast kuwa,sai jini yake yi,ƙiris ya rage ya 6alle,haƙika haroon ya cutar da ita,ya zalunce ta,Da mugunta yayi mata hakan,Dama babu Imani aranshi,duk ya faffasa mata skin ɗinta da Nails ɗinshi,saboda baya yanke akaifa,doguwar ƙumba ne dashi, Aunty babba tasha kuka,Tuntana kukan fili har ta koma yin kukan zuciya,wanda yafi ciwo,Sai da ta nemi taimako a hotel ɗin,sannan ta samu aka ɗauki hayaam,Suka kaita wani private hospital saidai sam bata sanar dasu haƙiƙanin abunda ya sameta ba don tasan karshe reporting za’ace ayi wurin yansanda ita kuma bata son asirinsu ya tonu har abun ya kai kunnan su Ishaq,tafi son in hayaam din ta farfado ta fadi wanda yayi mata hakan don ta tabbatar ba da karfi aka jata dakin ba don wanda ya kira ta ya sanar da ita halin da take ciki har sunan hayaam din ya ambata hakan kuma na nufin ya santa ne,

Tunda aka shiga da ita ciki,Likitoci suka taru akanta,Aunty babba na zaune zugudum saman waiting seat,tashin farko sae da suka fara kar6ar kuɗin gadon kusan Naira dubu 50,Sannan za’ayi mata aiki ciki da waje a ƙalla za’a cajesu kuɗi kusan Dubu ɗari biyar,Bayan haka akwai alluran da za’ayi mata ajikinta kuɗinsu ya kai kimanin dubu 20, Abun yayi matuƙar girgizata,ita babbar damuwarta,ba halin da hayaam ke ciki ba,Kuɗinsu da suke tattalawa zasu je wurin boka,Har an yashe kusan rabinsu,wasu mutanen dai ba imani aransu,ɗaya daga cikin halin ɗan adam kenan,Duk yadda take da hayaam same parents,Amma harta fara tunanin guduwa ta barta a asibitin saboda gudun kar su talauta ta,Kuma ta yanke shawarar zata yi ma Abra magana tazo su tafi wurin bokan tare da ita,Tunda ita hayaam ta gama lalacewa,babu wani amfanin da zata yi mata,ƙarshe ma taja masu asara,yini tayi a asibitin tana zirga zirga,Yayin da zuciyarta ke saƙa mata,ta gudu tabar asibitin,tun da ta samu ta biya mata kuɗin aikin Can su ƙarata,

Har wuraren ƙarfe Goma na dare,lokacin an kammala yiwa hayaam aikin,Amma bata farfaɗo ba,tsayawa Aunty babba tayi abakin ƙopar shiga ɗakin tana kallon hayaam dake kwance,hancinta na sanye da Oxygen, Komawa tayi saman waiting seat din,inda tabar handbag ɗinta,ɗaukar jakar tayi ta buɗe ta,biro ta curo tare da memo,aza takardar tayi saman kujerar sannan ta soma rubutu Kamar haka _Hayaam sae dai kiyi haƙuri,Wlh bazan iya cigaba da zama acikin asibitin nan ba,duk laifinki ne,Sai da na gargaɗeki akan karki kuskura ki ƙara kula wani ɗa namiji,amma da yake ke karyace ba’a raba ki da maza,Gashi nan kin jawowa kanki wanda yafi ƙarfinki,Ya gama dake yayi maki kankat,babu abunda yayi saura ajikinki balle har insa ran zakiyi mun amfani,Shiyasa na yanke shawarar zanyi ma Abra magana,zamuje wurin bokan tare da ita,Don bazan bari burina yaƙi cika ba har su Amani suyi nasara,In dana gode ma Allah bake kaɗai bace ƙanwar da nake da ita ba,Wlh dana ji kunya_ Tana kammala rubuta short note ɗin,Ta ɗauki handbag ɗinta,Sannan ta shiga cikin ɗakin da aka kwantar da hayaam ɗin,A gefenta ta ajiye wasiƙar,Sannan ta curo bandir ɗin kuɗi dubu hamsin ta ajiye mata a gefenta,a hankali ta furta Allah ya baki lafiya hayaam,Idan kuma kin riga mu gidan Gaskiya,Allah ya jiƙanki da rahama, Tana kai ƙarshen maganar,da sauri ta juya tabar ɗakin,batare da 6ata lokaci ba,ta gudu tabar asibitin, Rayuwa kenan,

*Boss Bature* ❤🤍❤Tunda sanyin safiya ringing ɗin wayarta ya farkar da ita daga bacci,cikin bacci takai hannu tana laluban wayar harta samu ta cafkota,janyota tayi cikin bargon tare da buɗe idanunta masu ɗauke da bacci,Sunan Mommy Azeema ne ya bayyana akan screen ɗin wayar,da sauri ta miƙe daga zaune,har time ɗin doguwar rigar jiyace a jikinta pink ɗin nan,picking call ɗin tayi ta kara wayar a kunnanta, “Assalamu alaikum,”On the other hand Aunty Azeema tace”Babyn Rafayet,kin tashi lafiya,” Murmushi sehrish ta ɗan yi tare da cewa”lafiya qalou Alhamdulillah,””Yawwa my Daughter,dama na kira ne about abunda ya faru a tsakaninki da Rafayet,” Natsuwa Sehrish tayi tana sauraronta Ci gaba da magana tayi,”Jiya na hana ki bashi haƙuri,Saboda nasan cewa yana cikin fushi,kuma haɗari ne ki tunkareshi a wannan lokacin,kafin nan abunda nakeso in sanar dake,duk yadda kike tunanin rafayet ba haka yake ba,mutunne shi mai ƙyanƙyami sosai,kuma yana da zuciya shiyasa a lokacin ranshi ya 6aci ne sosai,har yayi yunƙurin bugunki,kinsan in ran mutun ya 6aci zai iya aikata komai ba’a hayyacinshi ba,sae yadawo cikin hankalinshi kuma yazo yana danasani,Akwai ire irensu,Ni nasan ba ason ranshi yayi maki hakan ba,don ba halinshi bane wulaƙanta mace,Zuciya ce ta fisge shi har yayi wurgi dake,ya kuma yi yunƙurin marinki……”dakatawa ta ɗan yi da yin maganar na wani lokaci kafin ta ɗaura da cewa”Kin riga da kin faɗi abunda ke cikin ranki ba’a hayyacinki ba,ina mai tabbatar maki da cewar yanzu zai yi ƙoƙarin gyara mu’amularshi dake ne,Saboda ki daina yi mashi kallon mugu,Amma fa idan har kina son hakan ta faru dole sai kinje kin bashi haƙuri,sai daga baya na zauna nayi wani tunani,muddin baki bashi haƙuri ba,to akwai gagarumar matsala,tunda bai fara sonki ba,zai iya aikata komai daga ciki hada divorce tun kafin ma lokacin ya cika kin ga mu kuma ba haka muke so ba,Kuma idan kin bashi haƙuri ba hakan yana nufin cewa kin zubda ajinki bane,Darajarki zata ƙara daukaka a wurinshi,zai san cewa tabbas kina da hankali sosai tunda har kinsan kiyi laifi kuma ki nemi yafiya,kawai abunda nake so dake koda kinje bashi haƙuri karki nuna cewa ba’a hayyacinki kikayi maganar ba,”

Zuru sehrish tayi tana sauraronta,hankalinta yayi mugun tashi,Shin ta yaya zata tunkari Sgr da sunan zata bashi haƙuri? “Aunty azeema,still akwai matsala,Babban yaya ya hanani zuwa part ɗinshi fa,saboda period ɗin da nake yi,Nasan idan ya ganni zai tuna da jinin da ya gani ajikin wandona ƙarshema yayi mun korar kare in bai bugeni ba,”muryarta tamkar zata yi kuka haka tayi maganar, “Kada ki damu da wannan,In sha Allah babu abunda zai faru dake,sannan idan zaki je part ɗin nashi,ki gyara jikin naki sosai,Kuma ki shafe shi da turare” Gyaɗa kai kawai tayi tare da cewa”Shikenan zanje in sha Allah,duk yadda mukayi dashi zan sanar maki,” “Okey,saina ji ki,”Tayi rejecting kiran,Ajiye wayar sehrish tayi saman gadon,Saukkowa tayi tare da nufar toilet ta shiga,Cikin mintina tayi wanka ta fito jikinta sanye da undy taja shi saman ƙirjinta,hannunta ruƙe da Short towel,Goge ruwan jikinta tayi dashi,bayan ta kammala,ta zauna gaban mirror tana shafa body cream ɗinta,Bayan ta gama ta shafa powder afuskarta,tare da murza man baki,Comb ta ɗauka tana sharce gashin kanta, Turo kopar akayi,ta cikin mirror ta kalli wurin ƙopar don taga wanene,Jahad ce ta shigo hannunta ɗauke da plate meat balls ne aciki tare da Cup na coffee,

“Allah yasa nawa ne,”acewar Sehrish, Murmushi jahad ta saki tare da cewa”Naki ne mana,nayi tunanin ma baki tashi daga bacci ba,” tayi maganar tare da nufar wurin mirror ɗin ta tsaya,hannu tasa ta ɗauki meat ball din guda daya tace”Buɗe bakinki in saka maki,kiji idan yayi daɗi,” Buɗe baki Sehrish tayi,Jahad ta tura mata shi cikin bakinta,taunarshi ta shiga yi tana jinjina kai alamar daɗinshi yana kai mata karo, “Baby junaid nayi mawa,Ya kika ji ɗanɗanon”?.Sehrish tace”Bangane ba,wani junaid ɗin bayan basu nan?ko kin manta ne”? Jahad tace”Ae munyi waya dashi,Ya sanar dani cewa,Yau ko gobe zasu dawo,Amma basu duka ba,Shi dai yace bazai iya jure rashina ba,In ma basu dawo dashi ba,ko a ƙafa ne sai ya tako,”..fashewa da dariya Sehrish tayi,itama jahad ɗin dariyar ce akan fuskarta, “Gaskiya junaid na dabanne,yaci sunanshi Romeo,ga kuma juliet ɗinshi tsaye agabana,” Tayi maganar tana nuna Jahad dake atsaye,Murmushi jahad ta saki tare da cewa”Oh Ni sehrish,Wlh bansan ya zamu qare da junaid ba,idan munyi aure,Kina ganinshi ɗan ustazi ko,ba ƙaramin jarababbe bane,” Sehrish tace”gaskiya sai kin jure don kula da junaid ba abu bane mai sauki,a kwanakin baya can da jimawa,lokacin daya gane cewa ni mace ce,Mun ta6a yi dashi zamu haɗu a garden,Ni kuma na manta,kinsan Allah tun wurin magrib junaid ya zauna a garden ɗin nan yana jiran zuwana,maimakon da ya ji ni shiru ya dawo cikin gida,sae yaƙi shigowa saboda munyi alkawarin haɗuwa dashi,Ni kuma na manta,ɗan tahalikin nan,tsakar dare akayi ta nemanshi aka rasa,ashe yana can garden yana jirana,ga asthma ɗinshi ta tashi,da ace ban tuna ba naje wurin nan ba,da Allah kaɗae yasan abunda zai faru dashi…..”

Jin wannan maganar ba ƙaramin tayarwa jahad da hankali tayi ba, “Kice Majnun zan aura ba Romeo ba,junaid bashi da hankali wlh,”acewar jahad, Sehrish tace”yana da hankali mana,Junaid yana da mutunci sosai,ya kyautatamun sosai,bazan ta6a mantawa da halaccin da yayi mun ba,ina taya ki murna jahad,idan har kika auri junaid,babu ke babu yin aikin wahala,zan so naga rayuwar aurenku,tamkar comedy haka zata kasance,Zaki samu nishaɗi sosai,” Ba ƙaramin farin ciki jahad taji ba,sae faman sakin murmushi takeyi, Hannu sehrish tasa tare da ɗaukar cup ta kaishi bakinta tana kur6ar coffee,sae da ta shanye sannan taci gaba da ɗaukar Meatballs ɗin tana jefawa a bakinta,Duk jahad na atsaye ta ruƙe mata plate ɗin, “ki zauna mana,ƙafafunki basu ciwo ne”? “A’a,So nake in koma kitchen,Ina taya Aunty azmee aikin gida ne,” “Hosana fa?tunda mukayi sallar Asuba,dana koma bacci ban ganta ba lokacin dana farka,”tayi maganar a yayin da takai hannu gaban mirror,ta yago tissue tana goge bakinta, Jahad tace”Tana a dining,kinsan ta bata gajiya da ci,Ae ina tausayin Ya Omar,Don hosana saita ƙarar mashi da duk wani tattalin arziƙin da yake dashi,Gashi don ubanta ko girki bata wani iya ba,ci kawai ta sani,” Dariya Sehrish tayi sosai kafin tace”Sauƙinta ma,Ya Omar mutunne mai haƙuri,Kuma yana da kyakkyawar zuciya,Shi kaɗai ne zai iya control ɗinta,Amma fa zaiyi fama wlh,”tayi maganar tare da miƙewa ta koma gaban wardrobe,

Buɗewa tayi tana neman kayan da zata sanya ajikinta, Suna cikin magana,Hosana ta faɗo ɗakin tana kuka,bakinta cunkushe da Donuts,Ga wani a hannunta ta ruƙo,ɗayan hannun na ruƙe da wayarta, Juyowa sukayi atare suna kallonta,hankali atashe suka tunkareta har suna haɗa baki wurin cewa”Hosana,Me ya faru!me kikeyi ma kuka haka?Wani ne ya rasu”? Ɗaga masu kai tayi alamar eh,Gabansu ya faɗi rass,A sukwane suka kalli juna,kafin suka mayar da idanuwansu kanta, “Hosana faɗamun!waye ya rasu!”jahad tayi maganar jikinta na kerma, Sehrish tace”ki buɗe baki kiyi mana magana,ko wani ne bashi da lafiya,”? Sae lokacin ta taune donut ɗin bakinta tana matsar kwalla tace”Yayi Hatsarin Mota ya mutu”! Kallon juna sukayi atare kafin su kuma mayar da idanuwansu kanta,arazane suka haɗa baki wurin cewa”Wa?..cusa donut ɗin hannunta tayi acikin bakinta,Cikin shessheƙar kuka tace”wani Mai yin comedy,Yanzu nake gani acikin wayata,yayi hatsarin mota ya rasu” Sauke ajiyar zuciya su kayi atare,Duk atunaninsu wani ne ya rasu Cikin waɗanda suka tafi damaturu,

“Hosana ba kuka zakiyi mashi ba,Addu’a yakamata kiyi mashi don ita yake bukata,Allah ya jiƙanshi,Ya gafarta mashi zunubban shi,Allah yasa aljanna ce makomarshi,Amma idan kikayi mashi kuka to ke ba cikakkiyar masoyiyarshi bace,” “Nadaina kukan,Idan nayi sallah zanyi mashi addu’a,” ta ƙarasa maganar,tana cigaba da taunar donut ɗin dake a bakinta,sannan ta juya ta fuce daga ɗakin, Jiki asanyaye Jahad ta koma gefen gadonsu ta zauna,Sehrish kuma ta koma wurin wadrobe ɗin,Tana ɗaukar kayan da zata sanya, “Hosana ta tayar mun da hankalina sosai,Jikina duk yayi sanyi,” “Kin gane wa take nufi ne”?sehrish tayi mata tambayar,ayayin da take zura skirt ajikinta, “Kamal Aboki take nufi mana,Wanda yayi wannan comedy ɗin nan,na matar soja,yana rera waƙar india shi da wani,akwae ma wani wanda yake cewa gayuna kun ga Alert,su kuma sauran sai suce a’a,kin tuna shi”? Shiru sehrish tayi tana ƙoƙarin tuna comedy ɗinsa,can tace”Nagane shi,ya iya comedy sosai,Na ta6a ganin video ɗinshi a wayar Amrish,dayake ita mayyar kallon Comedy ce,Ni kinsan bancika amfani da waya ba,”

Jahad tace”naji mutuwarshi sosai,ya tsaya mun araina,rayuwar kenan kana taka Allah yana nashi,shiyasa wasu mutanen in suna aikata abunda suka ga dama har mamaki suke bani,sun manta cewa duniyar nan ba wurin zama bane,Jin daɗinta ƙalilan ne,da zarar ka mutu za’a kai ka grave ɗinka,daga kai sai Halinka,mai kyau ne ko mara kyau,idan na tuna cewa zan mutu in bar duniyar nan,ko inaso ko banso sai inji komai ya fita raina,ina rage duk wani dogon burin da nake dashi akan duniyar nan,Kuma ina ƙara kusanta kaina wurin Allah,…’ Sehrish tace”Wata rana muma babu mu,masu karanta labarin ma babu su,Mai bada labarin ma babu ita,Allah yasa dae mu cika da kyau da imani”_ Jahad ta amsa mata da”Ameen” sannan ta miƙe tare da nufar ƙopar fita daga ɗakin tana cewa”Ni zan wuce wurin Aunty azmee,kada mu barta da aiki ita kaɗae,” “Nima idan na kammala shiryawar zanzo na tayaku aikin”acewar sehrish,” Shaf shaf ta kammala shirya kanta,Cikin Skirt red colour,Asymmetrical Yana da baza ajikinshi,Gaban skirt ɗin bai kai bayanshi tsayi ba,yayi matuƙar yi mata kyau,Halter shirt ta sanya ajikinta white colour tayi tighting ɗinta,Red & white abun ba’a magana,Takalma ta zura a ƙafarta t-strap yana da ɗan tsini amma ba sosai ba,Launin skirt ɗinta ne,komawa tayi gaban mirror ɗin,ta ɗauki kwalbar turarenta tabi jikinta ta feshe ko’ina,saƙo da lungu,nan take ƙamshin ya gauraye ko’ina,bata sanya mayafi akanta ba,sai gashin kanta da yayi mata rumfa abayanta,

Fitowa tayi daga ɗakin,ta shiga cikin palour bata samu kowa ba,Suna can cikin gidan suna gyare gyare, Tunda ta hau saman staircases(matattakalar bene)gabanta ya shiga faɗuwa,lokacin da ta ƙarasa part ɗin nashi bata shiga daga ciki ba, Gabanta sae faɗuwa yake yi rass rass!leƙawa tayi ciki babu kowa Sae dae kayan abincin nan daya ci,’ Runtse idanuwanta tayi tare da ɗaga hannayenta izuwa saitin fuskarta, “Ya Allah Kana ganin baiwarka,acikin wani hali na firgici da tsoro,Allah ka tsare ni,Wllh idan naga ya nufo ni zai bugeni,Sae in watsa da gudu,Amma takalmana masu tsini ne,kada suja inyi tuntu6e in faɗi ƙasa,” Dakatawa tayi da yin zancen zucin nata,Sannan ta ɗan buɗe idanuwanta tana ƙara leƙa cikin palourn nashi, Jaraba yadda zata bashi haƙuri ta shiga yi, _babban yaya,Am sorry bazan ƙara ba,nasan nayi maka laifi,amma banyi hakan da niyyar na 6ata maka rai ba,Ba yin kaina bane,kuma ba hali na bane,Allah shine shaidata,ni bana yi ma na gaba dani rashin kunya,tsautsayine kawai da ƙaddara,A iya nan zan tsaya na baka haƙuri,saboda ka hanani shiga part ɗinka,har saina kammala period ɗina,Shiyasa bazan samu damar shigowa daga ciki in baka haƙuri ba_ Tana cikin tsara yadda zata sanar dashi,Kwatsam taji ƙamshin turarensa acikin hancinta,gabanta ne ya faɗi Rasss!waro ido tayi waje,ta zazzaresu,hankalinta yayi mugun tashi, Kasa juyawa tayi ta kalli bayanta,saboda tana da tabbacin cewar,SGR YANA TSAYE ABAYANTA!Ashe baya cikin part ɗin nasa,Tashin hankalin da ba’a sa mashi date! Ko ya sehrish zata ƙare!?

Sanƙamewa tayi a tsaye,ko motsi ta gaza yi,jira kawai take taji yayi wurgi da ita, “Excuse me,”muryarshi ce ta katseta,jiki na rawa taja gefe guda,yayin da idanuwanta ke kallon ƙasa taƙi yarda ta ɗago balle har su haɗa ido dashi,jikinshi na sanye da kaftan shirt har guiwa tare da trouser ɗinta brown colour,ya saki sumar kanshi ta baya,wani irin daddaɗan ƙamshine ke fitowa daga jikinshi,Slowly ya wuce cikin palourn batare da ya kalleta ba,abun ya yi matuƙar bata mamaki,tayi tsammanin tashin farko zai daka mata tsawa ne ya shako wuyanta,Sae gashi ko kallon inda take bai yi ba,Wuri ya samu saman Sofa ya zauna,tare da jingina bayanshi a jikinta, Tunani Sehrish ta shiga yi Ko ya ji abunda tace ko baiji ba Oho,Allah Wa’alamu,ranta ne ya bata cewar ta juya ta tafi kawai,tunda ba damar ta shiga ciki,ya riga da ya hanata,tana ƙoƙarin barin wurin,kwatsam taji yace”Zo nan,” Rasss taji gabanta ya faɗi,nan take taji fitsari ya matseta,daƙyar ta daure ta cije,ta dake sannan ta juya ta shiga cikin palourn,nesa dashi ta tsaya,saboda gudun kar ya shaƙota, Idanuwanshi na akan agogon hannunshi daya dafa sofa hand dashi, “Laifin me na aikata maki,da har na cancanci a kira ni,da mara IMANI mara TAUSAYI”?he said calmly, Wuƙi wuƙi sehrish tayi da ido,sae faman murza yatsun hannunta take yi,batasan amsar da zata bashi ba,

“Also,kinyi comparing ɗina da wannan fasiƙin mutumin,Why”? Shiru tayi tana ta faman mazurai,Miƙewa yayi daga zaunen da yake gadan gadan ya nufi wurinta,ja da baya Sehrish ta shiga yi tamkar ta watsa da gudu tabar falon sai dai ba dama,har saida suka ƙurewa bangon falon sannan ta tsaya,tare da ƙankame jikinta,tsoronta kada yace zai bugeta, Rumfa yayi mata da faffaɗan ƙirjinshi,duk tabi tasha jinin jikinta,Acikin zuciyarta sae faman ambaton La’ila ha’illah anta subhanaka inni kuntu minazzalimin takeyi,gaba ɗaya ƙamshin turaren jikinshi ya hanata sukuni,ga fargabar da ta shiga, “look at my face!nayi maki kama da mara tausayi,Mara imani”? Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,dakyar ta iya buɗe baki tace”A’a,“ “But Why u said so”?Girgiza kai ta shiga yi,batare da ta furta komai ba, “Shekarunki nawa”?Muryarta na kerma tace”Na shiga sha takwas,” Gwauron numfashi ya saki tare da zura hannunshi na dama cikin sumar kanshi a hankali ya furta”Ya Allah”!abun yayi mashi ciwo,ƙaramar yarinya na so ta caja mashi kwalwa, Zame hannun yayi daga cikin sumar,tare da dafe bangon da tafin hannun, “In my life,Wata ƴa mace bata ta6a gigin gaya mun magana ido cikin ido ba,batare jin shakkata ba,Sae ke,”yayi maganar yana nuna ta from head to toe, Hankalin Sehrish yayi mugun tashi,Hukuncin da zai yanke mata kawai take jira,”

“A ina kika samu ƙwarin guiwar yin hakan”?yayi tambayar yana kallon fuskarta, Shiru tayi,tana faman haɗiyar yawu, Jinjina kanshi yayi tare da ja da baya ya juya,Saman sofa ya koma ya zauna, “Come close”ya furta hakan yana nuna mata gefen table ɗin dake agabanshi, A hankali ta tako tazo gabanshi ta tsaya,sae lokacin ta ɗan saci kallon fuskarshi,karaf idanuwansu suka shiga cikin na juna,irin kallon da taga yanayi mata ne yasa tayi saurin duƙar da kanta ƙasa,ta ƙurawa takalman ƙafarta ido, “Don’t judge me,till u know me well,” Jinjina kanta tayi,batare da ta ɗago ba, “Idan har akwai abunda nake maki,Wanda yasa kike yi mun kallon wicked,mara tausayi mara Imani,lemme know,” Da sauri tace”babu komai,””I don’t trust u,If u can’t say it,ki rubuta mun a Text message” Abun yayi matuƙar ɗaure mata kai,yadda tayi tsammani ba haka ta gani ba,kokonto ta shiga yi anya Sgr ɗin da ta sani ne kuwa?kodae mafarki take yi ne,ta kasa yarda cewa da gaske ne shi yake yi mata, A hankali ta furta mashi toh,Juyawa tayi ta kama hanyar fita daga falon,tafiya take yi tana wasi wasi acikin zuciyarta, “Idan ina takura maki ne,Remain just 2 months na bar ƙasar,Zan sallame ki ne,kiyi rayuwarki kamar yadda kika saba,”. dakatawa tayi da yin tafiyar ta ɗan juya tare da kallonshi,

ba ita yake kallo ba,idanuwanshi na a lumshe,ci gaba da magana yayi”Ki dawo ki ci gaba,da yin aikin ki a part ɗina,” Tayi matuƙar yin mamakin abunda yace mata,hatta kalamansa ya tausasasu bakamar yadda yake yi mata magana ba ada, “Am waiting for my breakfast,then bedroom ɗina yana buƙatar gyara,” “Amma ka hanani yin aiki a part ɗinka ayanzu,” “Nayi cancelling,”Nauyayyiyar ajiyar zuciya ta sauke,ta wani 6angaren taji daɗi sosai,duk da bata ji daɗin kalaman da ta faɗa mashi ba a jiyan nan,da alama sun ta6a mashi zuciyarshi sosai, Komawa cikin falon tayi,gaban table ɗin sa taje,ta kwashe ledojin nan da aka kawo mashi na restaurant,Sannan ta juya ta nufi ƙopar fita daga falon,tana tafiya tana waiwayenshi har wani ƙara leƙen fuskarshi takeyi,Saboda abun ya ɗaure mata kai sosai,

Abban Sojoji Takun Karshe Chapter 92 – Hausa Novels (2024)

References

Top Articles
Latest Posts
Article information

Author: Zonia Mosciski DO

Last Updated:

Views: 6466

Rating: 4 / 5 (51 voted)

Reviews: 82% of readers found this page helpful

Author information

Name: Zonia Mosciski DO

Birthday: 1996-05-16

Address: Suite 228 919 Deana Ford, Lake Meridithberg, NE 60017-4257

Phone: +2613987384138

Job: Chief Retail Officer

Hobby: Tai chi, Dowsing, Poi, Letterboxing, Watching movies, Video gaming, Singing

Introduction: My name is Zonia Mosciski DO, I am a enchanting, joyous, lovely, successful, hilarious, tender, outstanding person who loves writing and wants to share my knowledge and understanding with you.